Martanin Shugabannin Duniya Bayan Harin Da Amurka Ta Kai Kan Iran
Martanin Shugabannin Duniya Bayan Harin Da Amurka Ta Kai Kan Iran Rubuce daga: Nuhu Saad Kumurya, CEO Kumurya Media Inc. Bayan da Amurka ta kai hari kan muhimman cibiyoyin nukiliya na kasar Iran, shugabannin duniya sun fara fitar da martani daban-daban da ke nuna ra’ayoyinsu kan wannan mataki mai cike da hatsari. Ga yadda wasu daga cikin manyan shugabannin suka bayyana: 🇮🇱 Firayim Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu “Ina taya shugaban kasa Trump murna. Shawarar da ka dauka ta kai hari kan cibiyoyin nukiliyar Iran da karfin iko da gaskiya na Amurka wani tarihi ne da zai sauya yanayin duniya... Tarihi zai rubuta cewa shugaban kasa Trump ya dauki mataki don hana wani mummunan gwamnati samun makaman da suka fi kowanne hadari a duniya.” 🇺🇳 Sakataren Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres “Ina nuna matukar damuwa game da amfani da karfin soja da Amurka ta yi a yau kan Iran. Wannan babbar barazana ce ga zaman lafiya da tsaron duniya... B...